Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano na shirin horar da matasa miliyan 1.5 a fannin fasahar zamani

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da shirin horar da matasa miliyan 1.5 a fannin ilimin fasahar zamani da ƙwarewar zamani domin rage zaman kashe wando da bunƙasa tattalin arziki.

Shugaban Hukumar Ci gaban Fasahar Sadarwa ta Jihar Kano KASITDA, Dakta Bashir Abdu Muzakkari, ya ce, shirin Kano State Digital Economic Policy and Digital Transformation Agenda zai gudana daga shekarar 2025 zuwa 2027, tare da raba matasan zuwa matakin asali, matsakaici da na ƙwararru.

Ya ce matasa 150,000 aka fara ɗauka a matsayin shirin gwaji, yayin da fiye da 1,100 suka kammala karatu daga cibiyoyin horo na jihar.

Haka kuma, an ƙaddamar da shirin Hackathon HEAT (Health, Education, Agriculture and Transportation) domin ƙirƙirar mafita da samar da ayyukan yi ga matasa.

Ƙungiyar KALM Community Initiative, wacce ke haɗin gwiwa da KASITDA, ta ce manufarta ita ce buɗe ƙofofi ga matasa a fannin fasahar zamani, tare da saukar da shirin zuwa ƙananan hukumomi da sauran sassan ƙasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!