Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta fara kwato motocin da wasu tsoffin kwamishinoni suka tafi da su

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta fara kwato motoci mallakin gwamnati da wasu tsofaffin kwamishinoni suka tafi da su bayan  yin murabus din su.

 

Shugaban Hukumar karbar korafi da yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano, Comrade Sa’idu Yahaya ne ya jagoranci aikin a yau Alhamis.

                                    

Ya ce ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Kano ya rubuta wasiku ga tsofaffin jami’an domin su mayar da motocin, amma suka gaza bin umarnin, lamarin da ya sa aka dauki matakin kwato su.

 

Daga cikin wadanda aka kwato motocin hannun su akwai tsohon Kwamishinan Tsaro, Air Vice Marshal Ibrahim Umar da tsohon Kwamishinan Matasa, Mustapha Rabiu Kwankwaso sai tsohon Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Ibrahim Kofar Mata da tsohon Kwamishinan Jin Kai Dakta Adamu Aliyu Kibiya, da tsohon Kwamishinan Ayyuka na Musamman, Nasiru Sule Garo.

 

Hukumar ta ce, za ta ci gaba da daukar matakai domin kare dukiyar gwamnati.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!