Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano ta fara zawarci masu zuba jari a bangarorin samar da wutar lantarki

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta fara zawarcin masu zuba jari a bangarorin samar da wutar lantarki da aikin gona da samar da ayyukan more rayuwa domin bunkasa tattalin arzikin jihar.

Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana haka, yana mai cewa, tuni suka fara tattaunawa da wasu masu sha’awar zuba jari a jihar.

Ya ce gwamnatin Kano ta yi alkawari wa masu samar musu da filaye da rage musu haraji da samar musu da tsaro da kuma kayayyakin more rayuwa.

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne yayin da yake gabatar da jawabi a wajen wani taron duniya da ake gudanarwa shekara-shekara karo na takwas kan zuba jari a birnin Dubai na hadaddiyar Daular Larabawa.

Cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na gidan gwamnatin Kano Aminu Yassar ya fitar, ta ce, gwamna Ganduje ya bukaci ‘yan kasuwa na kasa da kasa da su yi amfani da damar da gwamnatin Kano ta ba su domin zuba jari a jihar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!