Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta gamsu da aiyyukan Titin Kilomita 5 na Ajingi, Wudil da Takai

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana gamsuwar ta ga aiyyukan Titin Kilomita biyar dake gudana a kananan hukumomin Ajingi, Wudil da Takai da a baya al’ummar yankin suka yi fama da kalubalen hanyoyin.

Aikin titin Kilomita biyar na Ajingi wanda ya lakume sama da Biliyan uku a baya yana da ga cikin da aka kwace daga hannun dan kwangilar da ya fara shi sakamakon tsaikon da ake samu, kafin sake bayar da shi ga wani sabon dan kwangilar da ya ke ci gaba da aiwatar da shi bayan korafin da al’ummar a yankin suka yi.

Da yake jawabi ga kwamishina da ‘yan tawagar ma’aikatar  bibiya da lura da aiyyukan gwamnatin jihar Kano, daya daga cikin shugabannin al’ummar yankin na Ajingi, Alhaji Shehu Isa Ajingi, bayyana yadda aikin ke gudana ta re da yabawa gwamnatin jihar.

A nasa jawabin kwamishinan ma’aikatar Kwamred Nura Iro Ma’aji Sumaila, ya ce aiyyukan suna ci gaa da tafiya yadda ya kamata kuma za a kammala su a cikin watan Disamba kamar yadda gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya sa wa’adin kammalawa.

A lokacin ziyarar duba aiyyukan kwamishina Nura Iro Ma’aji Sumaila, tare da tawagar ma’aikatar sun duba aikin ginin Masallacin Jumma’a  na Rijiyar Gwangwan, dake  Jido, a karamar hukumar  Dawakin Kudu, da wasu sauran aiyyukan da ake gudanarwa wadan da ke  dab da kammaluwa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!