Labarai
Gwamnatin Kano ta yaye dalibai daurarru 62 mazauna gidan Gyaran Hali

Gwamnatin jihar Kano ta ce za ta cigaba da tallafawa daurarrun da ke zaune a gidajen gyaran halin musamman basu ilimi mai nagarta dan bunkasa rayuwarsu.
Sakataren Gwamnatin Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne ya bayyana hakan a wajen yaye dalibai 62 dake zaune a gidan gyaran halin.
Alhaji Umar Faruk Ibrahim ya kara da cewa zasu ci gaba da saka idanu kan yadda ake koyar da daliban dake zaune a gidajen gyaran halin na jihar Kano.
Shugaban da ke kula da gidajen gayran hali na jihar Kano Ado Inuwa ya ce gwamnatin ta yi abunda ya dace sakamakon daukar nauyin karatun na su da ta yi har su ka kammala.
Shugaban makarantar wacce aka kafa ta a gidan gyaran halin Kurmawa karkashin jagorancin DCC Mu’azu Tukur mai ritaya, ya ce karatun hadin gwiwa ne da makarantar SAS da gidan makama da KERD duka karkashin ma’aikatar ilmin jihar.
Akalla dalibai 62 da biyu ne aka yaye maza da mata da ya samu wakilcin hukomomi daban-daban.
You must be logged in to post a comment Login