Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kwara ta musanta mutuwar ɗan NYSC sakamakon zazzbin Lassa

Published

on

Gwamnatin Jihar Kwara ta musanta  rahotannin da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa wani ɗan bautar ƙasa ya rasa ransa sakamakon  kamuwa da zazzbin Lassa, a sansanin horas da matasa masu bautawa kasa  na jihar.

 

Wannan na cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Sakataren yada labarai na ma’aikatar lafiyar jihar Saad Hamdalat, bayan da ma’aikatar ta gudanar da binciken gaggawa.

 

Sanarwar ta ce, sakamakon binciken karkashin kwararriyar Likita Dr Khadeejah Kamaldeen, bai bayyana wata shaida ta samuwa ko yaduwar zazzabin  Lassa a sansanin NYSC din ba.

 

Haka kuma ba a samu wani ko wata da ake zargi da cutar ba, sai dai an ƙara tsaurara matakan   kariya ga yan bautar kasar a sansanin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!