Labarai
Gwamnatin mu na ɗaukar tsauraran matakai don shawo kan matsalar tsaro- Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ɗaukar tsauraran matakai domin shawo kan matsalar rashin tsaro da ke addabar Najeriya.
Ya ce, gwamnatin su ta himmatu wajen tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin sassan Najeriya.
Ta cikin wani sako Shettima ya ƙara da cewa, sabbin tsare-tsare da dabarun tsaro da gwamnati ke aiwatarwa sun haɗa da ƙarfafa rundunonin tsaro, inganta kayan aiki, da kuma haɗin gwiwa da ƙasashen waje domin yaƙi da ta’addanci da sauran laifuka.
Mataimakin shugaban ƙasar ya kuma jaddada cewa, duk da ƙalubalen da ake fuskanta, gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an kawo ƙarshen matsalar tsaro gaba ɗaya.
You must be logged in to post a comment Login