Labarai
Gwamnatin Najeriya ta fara kwashe yan ƙasarta daga Iran

Shugabar hukumar da ke kula da ‘yan Najeriya da ke ƙasashen waje (NiDCOM)Abike Dabiri ce ta bayyana hakan,inda tace jami’an Najeriya suna jira a kan iyaka domin karɓar ‘yan ƙasar da ke tserewa daga yaƙin Iran, tana mai cewa kawo yanzu babu ɗan Najeriya da ya mutu a yaƙin.
Gwamnatin Najeriya ta fara kwashe ‘yan ƙasarta daga Iran, inda jami’ai ke musu rakiya daga kan iyakar Armenia yayin da yaƙin Amurka da Isra’ila kan Tehran ke ci gaba da ƙamari.
Abike Dabiri-Erewa, a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X ranar Talata, ta ce ana raka ‘yan ƙasar da ke son barin ƙasar Iran ta hanyar kan iyaka.
You must be logged in to post a comment Login