Labarai
Gwamnatin Najeriya ta yi watsi da zargin Amurka

Gwamnatin Tarayya ta yi watsi da rahoton wasu ‘yan Majalisar Dokokin Amurka da suka zargi Najeriya da nuna wariya ta addini, tana mai cewa babu wata manufar gwamnati da ke goyon bayan tsananta wa kowace ƙungiyar addini. Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya bayyana haka yayin martani kan rahoton da aka miƙa wa Shugaba Donald Trump.
Rahoton ya biyo bayan binciken da kwamitocin Majalisar Wakilai ta Amurka suka gudanar kan zargin tsananta wa Kiristoci da matsalolin tsaro a Najeriya. Sai dai Gwamnatin Tarayya ta ce matsalolin tsaro da suka haɗa da ta’addanci, fashi da makami da rikice-rikicen ƙabilanci ba su da alaƙa da wata manufar wariyar addini.
Gwamnatin ta jaddada cewa kundin tsarin mulki ya tabbatar da ‘yancin addini ga kowa da kowa, tare da ƙara da cewa za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, tare da bunƙasa dangantaka mai kyau da Amurka ta hanyar diflomasiyya.
You must be logged in to post a comment Login