Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya ta sanar da ranar fara hukunta masu shigo wa ba bisa ka’ida ba

Published

on

Gwamnatin tarayya ta sanya ranar 1 ga watan Agustan bana a matsayin wa’adin fara bayar da tsattsauran hukunci ga baki ‘yan kasashen waje da suka wuce gona da iri.

 

Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai, bayan kammala  taron wayar da kan masu ruwa da tsaki kan manyan sabbin fasahohin da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya ta yi kan tafiye-tafiyen fasinja na kasa da kasa, a shalkwatar Hukumar da ke Abuja.

 

Ya kuma ce, tsarin biza ta zamani da aka kaddamar kwanan nan ya aiwatar da aikace-aikace sama da 14,000 a cikin makonni shida na farko da fara wa.

 

Ministan ya  kuma shaida wa mambobin jami’an  Ofishin jakadancin kasashen ketare cewa, su   gaya wa jama’ar  irin matakin da za’a rika dauka da zarar an karya dokar kasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!