Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya zata kafa kwamitin kolin da zai bada shawarwarin kirkire-kirkire fasahar zamani

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce zata kafa kwamitin koli da zai riga bata shawarwarin kan kirkire-kirkere fasahar zamani, don inganta bangare a fadin kasar nan.

Mataimakin shugaban kasa Ferfesa Yemi Osinbajo ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da manema labarai, bayan da ya kai ziyara gani da ido a cibiyoyin kere-keren fasaha daban-daban da ke a jihar Legas.

Ferfesa Osinbajo ya kuma ce, a halin yanzu akwai tsare-tsare da dama da gwamnatin tarayya ta bujiro da su a bangaren fasaha inda matasan kasar nan da dama za su amfana.

Ya Kara da cewa, bisa la’akari da abubuwan da ya gani a cibiyoyin fasaha a jihar Legas, kasar zata bi sahun manyan kasashen duniya da ke kere-kere a fadin duniya.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!