Labarai
Hayaniya ta barke a Majalisar Wakilan Najeriya

An samu hatsaniya a zaman da Majalisar Wakilan Najeriya ta gudanar kan gyaran dokar zaɓen ƙasar ta 2025.
Sashe na 60 na dokar, wanda ya tanadi aika sakamakon zaɓe ta hanyar laturoni kuma nan take, da kuma sashe na 84 da ya tanadi bai wa jam’iyyu damar fitar da ɗan takara, ne suka haifar da rikicin.
Hatsaniyar ta kaure ne bayan da kwamitin da majalisar ta kafa domin yin gyare-gyare kan dokar a watan Disamban da ya gabata, ya gabatar da rahotonsa a zauren majalisar.
Bayan gabatar da rahoton, shugaban kwamitin, Francis Waive, ya buƙaci majalisar ta amince da amfani da hanyar aika sakamakon zaɓe ta laturoni, tare da ci gaba da amfani da takarda a matsayin madadi idan an samu tangarɗa, kamar yadda Majalisar Dattawa ta amince.
Haka kuma, rahoton ya ƙunshi batun bai wa jam’iyyu damar fitar da ƴan takara ta hanyar zaɓen fidda gwani kai tsaye, ko tsarin wakilai, da kuma sulhu tsakanin ƴan takara.
Daga nan ne Kakakin Majalisar, Hon. Tajudeen Abbas, ya tambayi mambobin majalisar su bayyana ra’ayinsu na “e ko a’a”, lamarin da ya ƙara ɗaga hankula a zauren, inda ya buga hatimin majalisar bayan da ya ce waɗanda suka amince sun fi rinjaye.
Sai dai lamarin da bai yi wasu mambobin daɗi ba, musamman ƴan hamayya, inda suka fita daga majalisar a fusace tare da rera waƙar suka ga takwarorinsu na APC.
You must be logged in to post a comment Login