Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar Hisbah ta kama mabarata anan Kano

Published

on

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu mutum 10 da ake zargin mabarata ne tun a watan Satumbar da ya kare bayan da aka yi zargin cewar sun take dokokin hukumar na yin bara akan Titunan jihar nan.

Kakakin hukumar ta Hisba Lawan Ibrahim ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.

A cewar sa wadanda ake zargin sun hada da maza 3 da mata 7.

An dai kama wadanda ake zargin da yin barar a tituna daban-daban a wani samame da hukumar ta gudanar a cikin birnin Kano.

Haka zalika  an kama mabaratan ne akan Titunan da suka hada da Railway da State Road da dai sauran su.

Sai dai kakakin hukumar ta Hisbah ya ce bayan an tantance su daga bisani an sake su, da aka gano cewar sababbi ne wajen yin barar.

Rahotanni sun bayyana cewar an sami ragowar mabarata akan tituna tun bayan da hukumar ta Hisbah ta kaddamar da samame tare da kama su, don hana masu yin bara a jihar Kano

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!