Labarai
Hukumar ICPC na shirinta gurfanar da Nasir El-Rufai

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta sanar da shirinta na gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a gaban kotu a yau Talata 24 ga Maris.
Hukumar ta ce za ta gurfanar da shi tare da wani Joel Adoga a Babbar Kotun Tarayya da ke Kaduna.
A cewar sanarwar da ICPC ta fitar a ranar Litinin, ƙarar da ake yi wa El-Rufai ta ƙunshi tuhume-tuhumen da suka hada da karkatar da kadarorin gwamnati da mallakar kadarorin jama’a ba bisa ƙa’ida ba, da kuma halsata kuɗin haram. Hukumar ta ce an shigar da karar ne domin a bi diddigin zargin da ake yi.
Haka kuma, ICPC ta bayyana cewa akwai wata ƙara ta daban da aka shigar a Babbar Kotun Jihar wadda ta shafi El-Rufai da wani Amadu Sule.
A cikin wannan ƙarar, ana zarginsu da amfani da mukami ba daidai ba da damfara, yunƙurin aikata damfara.
You must be logged in to post a comment Login