Connect with us

Kaduna

Hukumar kula da jirgin kasa ta ce a mako mai zuwa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna zai koma aiki

Published

on

Hukumar kula da zirga zirgan jirgen kasa ta kasar nan, ta  ce, ta kammala gyare-gyare layin dogon Abuja- zuwa Kaduna.

A cikin sanarwar da mai magana da yawunta Callistus Unyimadu ya fitar, hukumar ta ce jirgin zai koma aikin jigilar fasinja a hanyar a mako zuwa.

Sanarwa ta ce hukumar ta yi aiki tukuru wajen tabbatar da kammala gyare-gyaren cikin tsanaki.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana asalin ranar da jirgin zai koma aiki ba.

Idan dai za iya tunawa, a ranar 26 ga watan Agusta ne dai jirgin ya tuntsure, inda wasu mutane da dama suka samu raunuka, lamarin da ya sa aka dakatar da aikin jirgin domin a yi gyara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!