Connect with us

Labarai

Hukumar NiMet ta fitar da sabon hasashen yanayi

Published

on

Hukumar lura da yanayi ta kasa NiMet, ta ce za’a samu saukar ruwan sama da tsawa na kwanaki uku daga yau Litinin zuwa Laraba a sassan jihohin Kano da Jigawa da Zamfara sai Kaduna da Bauchi da Yobe da kuma jihar Katsina.

Haka kuma, hukumar ta ce, za a samu yayyafi da yammacin wadan nan ranaku a jihohin Jigawa da Zamfara da Kano da Kaduna da Bauchi da Yobe da Katsina da Kebbi da kuma Adamawa da Taraba.

 

Hasashen ya kuma bayyana cewa za a iya samun saukar ruwan a kowanne lokaci cikin wadan nan ranaku a jihohin Bauchi da Jigawa sai Katsina da Kaduna da kuma jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!