Connect with us

Labarai

Hukumar NiMet ta fitar da sabon hasashen yanayi

Published

on

Hukumar Kula da yanayi ta kasa NiMet ta yi hasashen cewa za’a samu yanayin kwallewar Rana daga yau Litinin zuwa Laraba a wasu sassan kasar nan.

A cewar rahotan yanayin da NiMet din ta fitar a jiya Lahadi a birnin tarayya Abuja ta ce yankin Arewa zai kasance da mai zafi tare da gajumare na tsawan kwanaku Uku.

A kudancin Najeriya kuwa, ana sa ran samun tsawa da ruwan sama kadan kadan a wasu sassan jihohin Bayelsa da Rivers Akwa Ibom da Cross River

A yankunan Arewa ta tsakiya kuwa suma zasu fuskanci hasken Rana mai dauke kura da Kuma hazo.

Hukumar ta yi gargadin cewa kura da iska tana yawo a yankin Arewa ta tsakiya inda ta shawarci jama’a su dauki matakan kariya musamman masu fama da cututtukan numfashi irin su Asma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!