Connect with us

Labarai

Hukumar NiMet ta yi hasashen samun mamakon Ruwa da Tsawa

Published

on

Hukumar dake lura da hasashen masana yanayi ta kasa NiMet ta yi hasashen cewar za a samu ruwan sama mai karfi tare da Tsawa na tsawon kwanaki uku daga yau Litinin a sassan kasar nan.

 

NiMet ta bayyana hasashen nata ne cikin wata sanarwa da ta fitar a shafinta na Internet.

 

Sanarwar ta kuma ce, za a samu yanayin Chida da ruwan sama a jihohin Kano da Bauchi da Taraba da Kaduna da Kebbi da kuma Katsina.

 

Haka kuma, ta ce za a samu ruwan sama da tsawa a kwanaki ukun a jihohin Zamfara da Adamawa da Kebbi da Taraba da kuma Kaduna, sai Kogi da Niger da Benue da Plateau da Nasarawa da kuma birnin tarayya Abuja.

 

Yayin da jihohin kudu da suka hadar da  Lagos da Ogun da Ondo da Akwa Ibom da Cross River da Rivers da Delta da kuma Bayelsa za a samu saukar ruwan sama mai karfi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!