Connect with us

Labarai

Hukumar NiMet ta yi hasashen samun mamakon Ruwan sama da Guguwa

Published

on

Hukumar  hasashen yanayi ta Najeriya NiMet ta yi hasashen samun mamakon Ruwan sama da Guguwa mai karfi daga ranar Litinin Zuwa Laraba a fadin Ƙasa.

 

Ta cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar Lahadi a birnin tarayya Abuja, NiMet ta bayyana cewa ana sa ran samun iska hade da guguwa hadi da ruwan sama da safe a wasu sassan jihohin Sokoto, Kebbi, Zamfara, Taraba, Adamawa da Kaduna da ke yankin Arewacin kasar.

 

Hukumar ta ce ana sa ran guguwar iska mai ɗauke da ruwa da yamma ko da rana a wasu sassan Adamawa, Taraba, Borno, Jigawa, Yobe, Kano, Katsina, Gombe, Sokoto, Kebbi, Zamfara da Kaduna.

 

Ta cikin rahoton Nimet,  ce za a iya samun guguwa  da ruwan sama da safe a wasu sassan jihohin Neja, Filato da babban birnin tarayya FCT, yayin da sauran sassan yankin zai kasance cikin rana da gajimare kaɗan.

 

A karshe hukumar ta NIMET ta shawarci direbobi da su  kula da tuki domin akwai hatsari  a irin wannan yanayi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!