Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar SEMA ta tabbatar da mutuwar mutane 6 a jihar Katsina sakamakon mamakon ruwan sama da iska

Published

on

Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Katsina SEMA ta tabbatar da mutuwar mutane shida a jihar, sakamakon wani mamakon ruwan sama da iska mai karfi da aka tafka a daren alhamis din da ta gabata.

Shugaban hukumar ta SEMA Alhaji Aminu Garba Waziri ne ya tabbatar da hakan, lokacin da yake zantawa da manema labarai yau juma’a a Katsina.

Aminu Garba Waziri ya ce mamakon ruwan saman da aka tafka a daren jiya yayi sanadiyyar lalata gidaje sama da dari biyar.

Alhaji Waziri yace mutane hudu ne suka mutu a yankin Kukar Gesa yayinda mutane biyu kuma suka mutu a yankunan Shinkafi da kuma Modoji.

Shugaban hukumar na SEMA ya kuma ce mutum biyar ne suka samu raunuka a yankin Kukar Gesa, tare da lalata gidaje lamarin da ya haifarwa mutane da dama rasa matsugunan su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!