Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin tarayya ta sanya hannu a kwantiragin fiye da dala miliyan 6 da wani kamfanin China

Published

on

Gwamnatin tarayya ta sanya hannu kan wani kwantiragin Dala biliyan 6 da miliyan 68 da wani kamfanin kasar China don gina layin dogo daga garin Badin zuwa Kaduna, daga cikin aikin layin dogon da ya tashi daga Lagos zuwa Kano.

Wannan jawabi na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktar yada labaran ma’aikatar Sufuri Yetunde Sonaike ta bayan jiya a Abuja, tana mai cewa Ministan Sufuri Rotimi Amaechi ne ya sanya hannu kan yarjejeniyar don fara aikin na Badin zuwa Kaduna.

A cewar sanarwar ministan ya shaida cewa aikin zai kammala ne cikin wa’adin shekaru biyu zuwa uku, kuma ma’aikatar za ta samar da kudaden da ake bukata a cikin kasafin kudin bana da na badi.

Layin dogon zai bi ta garin Oshogbo zuwa Ilori zuwa Minna, yayin da wani layi guda daga Oshogbo zai bi ta Ado-Ekiti.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!