Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar tsaro ta Civil Defence ta gargadi dillalan man fetur kan boye man da wasu daga cikinsu ke yi

Published

on

Hukumar tsaro ta Civil Defence ta gargadi dillalan man fetur da su kuka da kan su kan boye man fetur da kuma karkatar da shi wanda a ka dauko shi musammam domin al’ummar Jihar Yobe.

Babban kwamandan hukumar shiyyar jihar ta Yobe Ayinla Taiye Olowo shi ne ya yi wannan gargadi yayin da yake zantawa da manema labarai a jiya Alhamis a garin Damaturu, inda ya ce duk wanda aka kama daga cikin su zai fuskanci fushin hukumar.

Ya ce matsalolin da ake ta samu na boye mai tare da karkatar dashi ya janyo matsalar karancin man da ake ta fama da shi lamarin da ya jefa al’umma cikin mawuyacin hali.

Haka kuma ya ce hukumar ta na sane da wasu gidajen mai da ke sayar da mai sama da farashin gwamnati cikin dare inda ya ce jami’an hukumar za su ci gaba da sanya idanu domin damke wadan da ke da wannan mummunar ta’ada.

Ya kuma bukaci al’umma a jihar ta Yobe da su kai rahoton duk wani gidan mai da yake boye mai ko kuma sayar da shi ba bisa ka’ida ba ga hukumar inda tayi alkawarin za ta hada hannu a da Jama’a wajen magance matsalar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!