Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

ICPC: zata rinka bibiyar kudaden da aka ware don yakar Covid-19

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci ta ICPC ta kafa wani kwamiti da zai ke bibiyar kudadan da aka ware domin yaki da cutar Corona.

Mai Magana da yawun hukumar Mrs Rasheedat Okoduwa ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta fitar a birnin tarayya Abuja.

Okuduwa tace gamayyar jamian ta hukumar ICPC zata saka ido game da yadda zaa rika raba kudaden tallafin cutar ta Corona da sauran taimakon da zaa bayar da kuma abubuwan da aka karba daga guraran al’umma domin yaki da cutar.

Okuduwa ta kuma jaddada matsayar hukumar ta ICPC na kira ga duk masu ruwa da tsaki a harkar ta cutar covid 19 da su nesanta kansu daga duk wani abu da zai sa su fada cikin ayyukan cin hanci da rashawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!