Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

INEC: ba zata amince da shaida ko daya a kotun sauraron zaben shugaban kasa

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC  ta ce ba za ta gayyaci shaida ko daya ba don kare ta a kotun sauraron korafe-korafen zaben shugaban kasa da ya gabata, wanda PDP da dan takararta Atiku Abubakar ke kalubalantar sakamakon.

PDP da Atiku Abubakar suna kalubalantar sakamakon zaben shugaban da aka gudanar ranar 23 ga watan Fabarairun da ya gabata, wanda INEC ta ayyana shugaba Muhammadu Buhari a matsayin wanda ya lashe.

PDP da Atiku Abubakar sun gabatar da shaidu guda 62.

Alkalin Kotun Justice Muhammad Garba ya bad a umarnin ci gaba da sauraron karar a yau Litinin, to amma Lauyan Buhari da APC Wole Olanipekun ya roki kotun ta ba shi damar gabatar da jawabi a gobe talata da karfe 2 na rana.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!