Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

INEC:za ta yi jinkirin baiwa wanda ya samu nasarar zaben gwamnan jihar Zamfara

Published

on

Hukumar zabe ta kasa (INEC), ta ce za ta yi jinkirin baiwa wanda ya samu nasara a zaben gwamnan jihar Zamfara da aka kammala a baya-bayan nan, takardar shaidar lashe zabe.

Haka zalika hukumar INEC ta kuma ce za ta yi jinkirin baiwa ‘ya’yan jam’iyyar ta APC da suka samu nasara a yayin zaben ‘yan majalisun dokokin jihar da aka gudanar a ranar tara ga watan da muke ciki na Maris takardar su ta lasisi.

Hakan na cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na facebook.

A cewar sanarwar hakan ya faru ne sakamakon karbar takardar kotu wanda rushe zaben fidda gwani da jam’iyyar APC a gudanar a jihar.

A shekaran jiya litinin ne dai kotun daukaka kara da ke Sokoto ta rushe zabukan fidda gwani da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar ta Zamfara.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!