Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Diyar ga mataimakin shugaban kungiyar editoci ta kasa ta shake iskar ‘yanci

Published

on

Hajiya Habiba Abdulsalam wacce ‘ya ce ga mataimakin shugaban kungiyar Editoci ta kasa Malam Suleman  Uba-Gaya wacce aka sace a kwanakin baya anan Kano, ta shaki iskar ‘yanci, kuma tuni aka sada ta da iyalan ta.

Da yake shedawa manema labarai kan mumunan labarin Alhaji Uba-Gaya ya ce ‘yar ta sa ta gudu daga hannun wadanda suka sace ta a daren ranar Asabar.

Mataimakin shugaban kungiyar Editoci ta kasan ya kara da cewar, masu satar mutanen sun sace ‘yar ta sa ne ranar Juma’a tsakanin  karfe 5 zuwa 6 na yammacin ranar.

A cewar Malam Suleman Uba-Gaya Dan Uwan Habiba ne ya kira wayar ta bayan da ya kasa samu ta kuma ki shiga, daga nan ne suka shiga nema, yayin da mintuna kadan bayan da tayi Magana da daya daga cikin ‘yan uwan ta, hakan ne ya sababa cewa wasu da ba’a san ko suwaye ba sun sace ta.

Mataimakin shugaban kungiyar Editoci ta kasa ya kara da cewar yana godewa jami’an ‘yan sanda da hukumomin tsaro, saboda namijin kokarin da suka yi wajen ceto ‘yar ta sa a hannun masu satar mutane.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!