Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jami’an DSS sun mamaye majalisar dokoki da safiyar yau

Published

on

Jami’an tsaro sun mamaye majalisar dokokin Najeriya da safiyar yau Talata.

Jami’an tsaro da suka rufe fuskokin na hukumar tsaro ta farin kaya DSS sun rufe majalisar dokokin, rahotanni sun bayyana cewa sun isa harabar majalisar ne da misalin karfe 6:00 na safiyar yau Talata.

Jami’an tsaron sun kuma hana ma’aikata da ‘yan majalisar da kuma manema labarai shiga cikin harabar majalisar.

Sai dai daga bisani bayan da ‘yan majalisar suka yi kokarin shiga cikin zauren majalisar, jami’an sun bude kofar bayan da aka yi ta turka-turka a tsakanin su.

Jami’an tsaron na DSS sun dai bude kofar ne da misalin karfe 8:15 yayin da suka kira ‘yan majalisar da su zo su shiga zauren.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!