Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wata kotu da ke Abuja ta baiwa sufeton yan sanda damar mika sammacin kotu ga Bukola Saraki

Published

on

Wata kotu dake yankin Lugbe a birnin Abuja ta bawa babban sufeton yansanda na Najeriya Ibrahim Idris damar sammacin kotu ga Shugaban majalisar dattijai Bukola Saraki.

A wasikar da kotun ta bawa babban Sufeton Yansandan ta hanyar Barrister Oluwatosin ojaomo an nemi babban Sufeton Yansanda da ya mikawa Bukola Saraki tuhumar da ake yi masa data shafi aikata laifuffuka.

Barrister Oluwatosin ya zargi Bukola Saraki da kin mutunata gayyatar da babban sufeton yansandan kasar nan yayi masa ranar 24 ga Watan Yuli na shekarar bana da kuma hana binciken laifuffuka da kuma kin biyayya ga babban jamii dake aiwatar da aikin da doka ta bashi damar yayi wanda yace hakan laifi ne karkashin sashi na 136 da 149 na kundin Penal Code

An saka ranar 10 ga watan Satumba na bana domin fara shariar.

Rundunar yansandan kasar nan ce dai ta gayyaci Sanata Bukola Saraki da yayi mata bayani akan fashi da aka aikata a garin Offa na jahar Kwara a watan Afrilun shekarar da muke ciki inda aka zargi shugaban na majalisar dattijai da Gwamnan jahar Kwara Abdulfatah Ahmad.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!