Labarai
Jami’an Hukumar ICPC sun kai samame gidan Nasir El-Rufai

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta kai wani samame na bazata gidan tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da ke Babban Birnin tarayya, Abuja.
Rahotanni sun bayyana cewa jami’an hukumar sun isa gidan tsohon gwamnan ne domin suka gudanar da bincike na tsanaki a cikin gidan.
Wannan samame na zuwa ne kwana guda bayan da aka samu rahoton cafke shi da Hukumar DSS ta yi.
Ko da yake hukumar ICPC ba ta fitar da cikakken bayani kan abin da take nema ba, sai dai ana kyautata zaton binciken yana da alaka da zargin karkatar da kuɗaɗen jama’a da kuma wasu kwangiloli da aka bayar a lokacin mulkinsa.
You must be logged in to post a comment Login