Connect with us

Labarai

Jami’an tsaro sun daƙile hare-haren da yan Boko Haram suka kai a Maiduguri

Published

on

Hadin gwiwar jami’an tsaro sun daƙile wasu hare-haren da ake zargin ’yan ta’addar Boko Haram sun kai a yankin Ajilari Cross -Kofa a Maiduguri da kuma Karamar Hukumar Damboa ta Jihar Borno a daren wayewar Litinin. 

 

Hakan  na cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya fitar a yau Litinin.

 

Sanarwar ta bayyana cewar  jami’an tsaro sun isa yankin Ajilari Cross zuwa Kofa domin duba halin da ake ciki tare da ɗaukar matakan da suka dace bayan rahoton wani hari da aka dakile. 

 

A wani lamari na daban a Karamar Hukumar Damboa, jami’an tsaro sun dakile wani hari da aka kai da misalin ƙarfe 1 na dare, inda daga bisani aka dawo da zaman lafiya, a yankin.

 

Haka kuma, Gidan rediyon Dandalkura da ke birnin na Maiduguri ya ruwaito cewa jiragen saman Sojin Najeriya sun kai dauki yayin da aka ji karar harbe-harben bindiga a wasu sassa na birnin Maiduguri, lamarin da ya janyo firgici a tsakanin wasu mazauna yankunan kafin daga bisani lamarin ya lafa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!