Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jam’iyyar APC bata da ‘yan takarar gwamna da ‘yan majalisu a Rivers da Zamfara

Published

on

Babu ‘yan takaran gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin tarayya na jam’iyyar APC a jihohin Rivers da Zamfara a cikin jerin sunayen wadanda za su tsaya takara ga jam’iyyu daban-daban da hukumar zabe ta kasa INEC ta fitar a jiya Alhamis.

Hukumar ta INEC ta ce tun da fari wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta haramtawa jam’iyyar APC fitar da ‘yan takara a jihohin Rivers da Zamfara sakamakon rikicin da ya dabai-baye ta a jihohin biyu.

Haka zalika a cikin jerin sunayen mai dauke da sa hannun sakatariyar hukumar ta INEC Rose Oriaran Anthony, babu sunan wanda zai tsayawa jam’iyyar SDP takarar shugaban kasa.

A cewar hukumar ta INEC jam’iyyar ta SDP ba ta da cikakken dan takara sakamakon hukuncin kotu da ta haramta bayyana suna tsohon Gwamnan jihar Rivers Donald Duke a matsayin wanda zai tsayawa jam’iyyar ta SDP takarar shugaban kasa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!