Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dan takarar shugabanci a jami’yyar PDP ya jaddada matsayarsa na sayar da kamfanin NNPC da zarar ya samu nasarar lashe zabe

Published

on

Tsohon mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar ya kara jaddada matsayar sa na cewa matukar ya samu nasara a zaben shugaban kasa da za a yi a bana zai sayar da kamfanin mai na kasa NNPC.

Atiku Abubakar ya bayyana hakan ne a Lagos lokacin da ya ke ganawa da wasu kungiyoyin ‘yan kasuwa a jiya Laraba.

A cewar sa tun yana mataimakin shugaban kasa ya shawarci shugaban kasa na lokacin Olusegun Obasanjo game da sayar da kamfanin na NNPC sai dai ya ki amincewa da sharar sa.

Atiku Abubakar ya ce da an sayar da kamfanin na NNPC tuntuni da yanzu kamfanin ya tsaya da kafar sa.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma sha alwashin bunkasa kasafin kudin kasar nan matukar aka zabe shi, yana mai cewar tattalin arzikin Najeriya ka iya kaiwa dala tiriliyan daya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!