Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jarumar Kannywood Hawwa Maina ta rasu a asibitin koyarwa na Aminu Kano

Published

on

Fitacciyar jarumar shirin fina-finan kannywood Hauwa Maina ta rasu a asibitin koyarwa na Aminu Kano a daren larabar da ta gabata.

Marigayiya Hauwa Maina ta rasu ne sakamakon fama da ta yi da rashin lafiya ana kuma saran binne gawarta yau Alhamis a juhar Kaduna.

Hawwa Maina dai jaruma ce da ta yi fice a masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood, ta kuma lashe kyaututtuka a shekarar 2007 da 2010.

Marigayiya Hawwa Maina wadda ‘yar asalin garin Biu ce da ke jihar Borno an haifeta ne a garin Kaduna sannan ta yi karatun firamare a garin Geidam da da ke jihar Yobe da Kaduna, kafin daga bisani ta kammala karatun  Sakandire a Nguru da ke jihar ta jihar Yobe.

Haka zalika ta kuma yi karatun Diploma a bangaren gudanarwa a Kwalejin kimiyya da fasaha ta Kaduna wato Kaduna Polytechnic. Ta mutu ne ta bar ‘ya guda mai suna Maryam Bukar Hassan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!