Labarai
Jihar Neja ta bi sahun sauran Jihohi wajen samar da sabbin matakan tsaro
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/09/Sani-Bello.jpg)
Gwamnan jihar Neja Abubakar Sani Bello, ya fitar da sabbin matakan tsaro wanda ya hada da rufe manyan kasuwannin da ke ci mako-mako a fadin jihar.
Kazalika Gwamnatin ta taƙaita lokutan babura inda masu babur za su riƙa hawa daga karfe 6 na safe zuwa karfe 6 na yamma. Sannan kuma an hana motocin ita ce zirga-zirga a fadin jihar.
Sakataren Gwamnatin jihar Ahmed Ibrahim Matane ya yi ƙarin bayani a kai, inda yace hakan zai taimaka wajen inganta tsaro a jihar.
Wannan dai na zuwa ne kwanaki bayan da jihohin Kaduna, Katsina da Zamfara suma suka sanar da ɗaukar wannan mataki.
You must be logged in to post a comment Login