Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jihar Neja ta bi sahun sauran Jihohi wajen samar da sabbin matakan tsaro

Published

on

Gwamnan jihar Neja Abubakar Sani Bello, ya fitar da sabbin matakan tsaro wanda ya hada da rufe manyan kasuwannin da ke ci mako-mako a fadin jihar.

Kazalika Gwamnatin ta taƙaita lokutan babura inda masu babur za su riƙa hawa daga karfe 6 na safe zuwa karfe 6 na yamma. Sannan kuma an hana motocin ita ce zirga-zirga a fadin jihar.

Sakataren Gwamnatin jihar Ahmed Ibrahim Matane ya yi ƙarin bayani a kai, inda yace hakan zai taimaka wajen inganta tsaro a jihar.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki bayan da jihohin Kaduna, Katsina da Zamfara suma suka sanar da ɗaukar wannan mataki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!