Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano: An yi jana’izar mutanen da suka rasu sakamakon fadan Daba

Published

on

An gudanar da zana’izar wasu mutane biyu da suka rasa ransu a daren jiya Lahadi sakamakon faɗan daba a yankin unguwannin Yakasai da Rimi da Kofar Mata da kuma Zage.

Rahotonni sun bayyana cewa, a daren jiya ne wasu bata garin matasa suka farmaki mutane sakamakon fadan daba da suka tayar.

Sai dai har zuwa safiyar yau Litinin mazauna yankin Yakasai na zaman ɗar-ɗar sakamakon yadda faɗan daban ya sake tashi.

Freedom Radio ta kai ziyar ganin da ido da safiyar Litinin din nan inda ta tattauna da wasu mazauna yankin inda suka bayyana cewa rikicin ya samo asali ne daga kallon kwallon kafa a filin wasa na Kofar Mata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!