Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Karya lagon boko haram ne ya sanya aka samu nasarar kubutar da yan matan chibouk-shugaba buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce karya lagon kungiyar Boko Haram ne ya sanya aka samu nasarar kubutar da yan matan chibouk 106 da kuma na sakandare Dapchi 104 wadanda mayakan na boko haram suka sa ce a baya.

Shugaba Buhari ya bayyana haka ne da safiyar Talatar nan lokacin da yake jawabi ga al’ummar Najeriya a wani bangare na bikin ranar dimokuradiyya ta bana da ke gudana a yau.

Ya kuma ce gano lago da maboyar yan Boko haram din shima ya taimaka wajen kubutar da sama da dubu goma sha shida da ke tsare a hannun mayakan na Boko Haram.

Ya ce kafin ya kama aiki a matsayin shugaban kasa ya iske kungiyar ta Boko haram ta kame garuruwa da dama da tambayar dasu karkashin ikon ta a yankin arewa maso gabashin kasar nan.

Muhammadu Buhari ya kuma yi alkawarin cewar gwamnatin sa ba zata huta ba har sai ta tabbatar da kakkabe dukkanin ayyukan yan ta’adda a kasar nan baki daya.

Ya kuma yiwa al’ummar kasar nan fatan alheri a lokacin da suke gudanar da bukukuwan ranar dimokuradiyya na bana.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!