Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kasashen duniya su kawo mana dauki kan sha’anin tsaro – Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bukaci kasashen duniya da su tallafawa Najeriya wajen kawo karshen matsalolin tsaro da ayyukan cin hanci da rashawa har ma da tabarbarewar tattalin arziki.

Wannan dai na cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan kafafen yada labarai Femi Adesina ya fitar a Abuja.

Sanarwar na bayyana cewa, shugaba Buhari ya yi wannan kira ne lokacin da yake karbar shaidar kulla yarjejeniyar Diplomasiyya da wasu kasashen duniya.

Cikin jakadun kasashen da suka ziyarci fadar ta shugaban kasa akwai jakadan kasar Gambia Muhammad Njie, da na Korea ta Kudu Kim Young-Chae da kuma na kasar Slovakia Tomas Felix.

Sauran sun hada da: jakadan kasar Bangladesh Masudur Rahman da na Austrelia John Donnelly da na kasar Guinea Bissau Dr Jaao Butiam.

Ta cikin sanarwar Buhari yace akwai bukatar daukar matakai a tsakanin kasashen duniya domin a hada hannu guri guda don kawo karshen matsalolin dake addabar duniya musamman ayyuakan ta’addanci a sassa daban-daban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!