Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta bukaci Ganduje ya biya Sarki Sunusi diyyar miliyan 10

Published

on

Wata babbar kotu a birnin tarayya Abuja a ranar Talata, ta nemi gwamnatin jihar Kano da ta nemi afuwa a wajen tsohon sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi na biyu a wasu jaridun Najeriya guda 2.

A hukuncin da kotun ta zartar bisa jagorancin mai shari’a Anwuli Chikere ta ce, tilastawa fitar da sarkin daga jihar bayan cire shi daga muƙamin sa ya saɓa da tsarin mulki da kuma haƙƙin sa na dan adam.

Don haka gwamnatin jihar Kano da ta biya sarkin naira miliyan 10 saboda ɓatanci da aka yi masa.

Idan za a iya tunawa dai, gwamnatin ta sauke sarkin daga muƙamin sa a ranar 9 ga watan Maris na shekarar 2020, bayan an zarge shi da rashin yin biyayya ga gwamnati.

Bayan cire shi ne sarkin ya je kotu domin a binciki halaccin tsare shi da aka yi a ƙauyen loko da ke jihar Nasarawa.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!