Labarai
Kotun daukaka kara ta rushe hukuncin da kotun tarayya ta yi kan hana gudanarda zaben Kananan Hukumomi a Kano

Kotun daukaka kara ta rushe hukuncin da kotun tarayya ta yi kan hana gudanarda zaben kananan hukumomin a jihar Kano
Mai shari’a Oyewumi, JCA, ita ce ta karanta hukuncin, Kotun ta yanke cewa Kotun Tarayya ba ta da hurumin sauraron ƙarar da masu ƙara suka shigar. Saboda haka ta yanke hukunci ne da goyon bayan ƙorafin da aka shigar.
Kotun ta yanke hukunci, tare da rusa hukuncin da Kotun Tarayya ta yanke a baya.
Gwamnnatin jihar kano da Majalisar dokokin kano da Hukumar zabe ta jihar Kano suka daukaka kara kan Hukuncin Babbar kotun tarayya data hana gudanar da zabe da rushe shugabanin Hukumar.
You must be logged in to post a comment Login