Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar al’ummar Musulmin jihar Lagos ta bukaci Samar da kotun shari’ar mulsunci

Published

on

Kugiyar al’ummar Musulmi da ke jihar Lagos ta buka ci da a samar da kotun shari’ar musulunici da za ta dinga shari’a kan al’amuran da suka shafi addinin musulunci.

Kugiyar na mika wannan bukata ne a lokacin da suke tattaunwa da dantakar Gwamnan jihar a jam’iyyar AD mista Owolabi Salis a jiya laraba.

A cewar kugiyar al’ummar musulmi na bukatar a gina musu kotun addinin musulunci, duba da cewa a yanzu haka al’amaran musulmi na hannun wadanda ba musulmi ba ne a jihar, inda ya ce mafiya yan lokuta ba sa samun adalci.

Da ya ke maida jawabi Owolabi Salis Ya ce matukar aka zabe shi a matsayin gwamnan jihar to kuwa zai kafa kwamitin da zai duba yadda  za a samar da kotun domin amfanin al’ummar musulmin jihar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!