Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar dattawan Arewa na kalubalantar dan takarar shugabanci na jam’iyyar PDP

Published

on

Dan majalisar a jamhuriya ta daya kuma mamba a kungiyar dattawan Arewa Dr, Junaid Muhammed ya ce kungiyar ba ta amince da goyawa dan takarar jam’iyyar PDP Atiku baya ba a yayin babban zaben da za’a yi a ranar Asabar mai zuwa.

A cewar Dr, Junaidu wasu daga cikin ‘yan kungiyar dattawan Arewa ne wanda Ango Abdullahi ke jagoranta suke marawa dan takarar shugaban kasar baya ba duka ‘yan kungiyar ba.

 A dai makon da ya gabata ne wasi dattawan Arewa suka sanar da cewar za su marawa Atiku Abubakar baya a yayin zaben ranar 16 ga wannan watan na Fabarairu.

Hakan na ya biyo bayan taron da kungiyoyin dattawa suka gudanar a Abuja mai taken ‘’Taron shugabanni da dattawan Najeriya a inda kungiyoyin Ohaneze Ndigbo da Pan Niger Delta da Middle Belt da kuma tsagen kungiyar Afenifere suka yi don bayyana dan takarar da suke goyan baya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!