Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar matasan Janbulo, sun bukaci matasa da su dai na yarda ana amfani da su yayin zabe

Published

on

Kungiyar Janbulo Youth Forum ta yi kira ga matasa da su dai na yadda ‘yan siyasa na amfani dasu wajen ta da hankular jama’a domin biyan bukatun kansu na siyasa.

Sakataren kungiyar kwamared Abubakar Muhammad Sa’id ne ya bayyana haka, yayin wani gangamin wayar da kan matasa kan illolin tada hankulan jama’a da kungiyar ta gudanar jiya a yankin.

Ya ce wajibi ne al’umma da su sanya ido kan duk dan siyasar da su ka ga yana neman lalata tarbiyar matasa.

Wasu matasa da suka kasance a wajen taron sun bayyana irin darusan da suka koya a yayin taron.

Wakilin mu Bilal Nasidi Mu’azu ya rawaito cewa, kungiyar ta jaddada kudirinta na ci gaba da wayar da kan matasa dake lungu da sako na jihar Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!