Connect with us

Kaduna

Kungiyar Dattawan Arewa sun yi Allah wadai da kalubalen tsaro da ya ke addabar yankin

Published

on

Kungiyar Dattawan Arewacin kasar  nan, sun yi Allah wadai da kalubalen tsaro da ya ke addabar  yankin, inda suka yi kira da a dauki kwararan matakai don magance matsalar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, kakakin kungiyar Abubakar Jiddere, ya yi Allah wadai da tabarbarewar tsaro da ake samu, dama kawo tasgaro ga tattalin arzikin a yankin.

Dattawan, sun kuma bukaci gwamnonin jihohi da su ba da hadin kai, tare da yin kira ga jami’an tsaro da su kawo karshen  matsalar rashin tsaro da ya ke addabar arewacin kasar.

Abubakar  Jiddere, ya bayyana matakan da aka dauka na farfado da tattalin arzikin Arewa, tare da neman hadin kan  alummar yankin domin  kawo karshen matsalar rashin tsaro a arewacin kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!