Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi NULGE ta yi barazanar gudanar da zanga-zangar gama gari

Published

on

Kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi ta kasa NULGE ta yi barazanar gudanar da wata zanga-zangar gama gari matukar majalisun dokokin jihohi dana tarayya suka yi watsi da dokar baiwa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin Kansu.

Shugaban kungiyar reshen jihar Kano Comrade Abdullahi Muhammad Gwarzo ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai yau.

Ya ce ko kadan ‘yayan kungiyar ba za su amince da ci gaba da kasancewar kananan hukumomi karkashin ikon jihohi ba.

Comrade Abdullahi Muhammad Gwarzo ya kuma nuna rashin jin dadin sa game da rahotannin da ke nuna cewa majalisar dokokin Kano taki amincewa da dokar.

Kungiyar ta kuma sha alwashin daukar wasu matakai masu tsauri matukar aka ki baiwa kananan hukumomin damar sarrafa kudaden su kamar yadda jihohi da gwamnatin tarayya ke yi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!