Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Shugaban hukumar hana fasakauri ya ce masu kokawa ga gwamnatin Buhari ragwaye ne

Published

on

Shugaban hukumar hana fasakauri ta kasa wato Kwastam kanal Hameed Ali mai ritaya ya ce mafi akasarin ‘yan Najeriya da ke kukan yunwa a karkashin gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ragwaye ne, da basu da karfin zuciyar tashi domin neman na kansu.

 

Shugaban na Kwastam ya bayyana haka ne, yayin da ya ke karin haske dangane da nasarorin shirin gwamnatin tarayya kan bunkasa ayyukan noma a kasar nan, a wata ganawa da yayi da kungiyar magoya bayan shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a fadar gwamnati da ke Abuja.

 

A cewar Hameed Ali, babu yadda za ayi abinci ya rika fadowa mutane daga sama, dan haka ya zama tilas mutane su tashi tsaye domin amfani da damar su wajen neman abin rufawa kai asiri.

 

Dangane da shugabancin Buhari kuwa, shugaban na kwastam ya ce kaunar Najeriya da ‘yan kasar ne ya sanya shi fafutukar karbar jagorancin kasar duk da cewa shekarun sa sun haura 70.

 

Ali ya kara da cewa inda shi ne ya ke da yawan shekarun shugaba Buhari, ga fansho mai kyau da gidan sa na zama a Daura, ba zai dorawa kan sa nauyin da zai hanashi sararawa ba ta hanyar shiga siyasa, amma kaunar kasar sa ta sa shugaba Buhari yanke wannan shawara.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!