Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kungiyoyin ma’aikata ta bukaci majalisun dokoki da su yi watsi da mafi karancin albashin naira dubu ashirin da bakwai

Published

on

Kungiyoyin ma’aikata da dama sun bukaci majalisun dokokin tarayya da su yi watsi da kudirin dokar mafi karancin albashi na naira dubu ashirin da bakwai da fadar shugaban kasa ta turawa musu a jiya.

A wasu sanarwar da su ka fitar daban-daban, Kungiyar manyan ma’aikatan gwamnati ta (ASCSN), da kuma kungiyar malaman makaranta ta (NUT) sun bukaci majalisun biyu da su amince kawai da mafi karancin albashi na naira dubu talatin. 

Kungiyoyin sun dage kan cewa babu gudu ba ja da baya game da zancen mafi karancin albashi na naira dubu talatin.

A jiya ne dai babban mataimakin na musamman ga shugaban kasa kan harkokin majalisar dattawa Sanata Eta Enang ya tabbatar da cewa, fadar shugaban kasa ta mika da kudirin dokar ga majalisun dokokin tarayya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!