Labarai
Kwalejin Barewa zata cika shekara 100 da kafuwa
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/10/EO496eyX4AAVVAr.jpg)
Kungiyar tsoffin daliban kwalejin Barewa sun gudanar da taron tattaunawa kan yadda za su gudanar da bikin cikar kwalejin shekaru dari da kafuwa nan da makwanni biyu.
A yayin taron shugaban kungiyar Alhaji Nasir Ibrahim Dantiye ya ja hankalin daliban dake karatu a yanzu da su guji aikata laifin satar jarrabawa.
Dantiye ya ce satar jarrabawa na daya daga cikin abinda ke sawa mutum ya rasa albarka a karatun da yake.
Sai dai ya ja hankalin iyaye da su rika kula da tarbiyyar “ya”yansu musamman wajen sauke nauyin da Allah ya dora musu.
An kafa kwalejin ta Barewa a shekarar 1921 inda a shekara mai kamawa ta 2021 kwalejin za ta cika shekara 100 da kafuwa.
You must be logged in to post a comment Login