Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kwamitin gudanarwar Jam’iyyar APC ta jihar Lagos ta dage zaben fid da gwani

Published

on

Kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC na kasa ya da’ge zaben fid da gwani na gwamnan jihar Lagos wanda tun da fari a shirya gudanarwa a yau Litinin.

 

Haka kuma jam’iyyar ta sauya ranar da za a gudanar da zabukan fitar da gwani na gwamna a jihohin Enugu da kuma Adamawa.

 

APCn ta kuma canja tsarin gudanar da zabukan jihohin biyu wato Enugu da Adamawa daga zaben delegate zuwa zabe ‘yar tinke.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa Yekini Nabena.

 

A cewar sakataren yada labaran jam’iyyar ta APC a yanzu, za a gudanar da zaben fid da gwani na gwamnan jihar Lagos ne a gobe Talata, yayin da a ranar Alhamis hudu ga wata za a gudanar da na jihohin Enugu da Adamawa.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!