Connect with us

Labarai

Kwara: An tura karin Yan Sanda yankin Kaiama domin karfafa tsaro da zaman lafiya

Published

on

Rundunar ’yan sandan Jihar Kwara ta tura karin jami’an tsaro zuwa yankin Kaiama domin karfafa tsaro da tabbatar da lafiyar mazauna yankin da matafiya bayan fashewar Bam.

 

Hakan  na cikin sanarwar da Jami’ar Hulda da Jama’a ta rundunar ’yan sandan jihar SP Adetoun Ejire Adeyemi ta fitar a jiya Litinin.

 

Sanarwar ta bayyana cewa an dauki matakin ne bayan fashewar bam a yankin, inda aka kara kaimi wajen sa ido da sintiri domin dakile duk wata barazana.

 

Haka kuma, rundunar ta bukaci al’umma da su kasance masu bin doka tare da kai rahoton duk wani abu da ba su gamsu da shi ba ga jami’an tsaro domin daukar matakin da ya dace.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!