Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ma’aikatan lafiya 7 sun kamu da Coronavirus a Borno

Published

on

Gwamnatin jihar Borno ta ce jami’an lafiya 7 ne suka kamu da cutar Covid-19 a jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar kuma sakataren kwamitin yaki da cutar Covid-19 na jihar Salihu Kwaya-Bura ne ya bayyana hakan a ranar jumu’ar nan, yayin taron bayar da bayanai kan halin da ake ciki game da annobar a jihar.

Jaridar Premium Times ta rawaito kwamishinan ya ce yanzu haka an samu mutum 15 da suka kamu da cutar, inda 2 daga ciki suka rasu.

Sannan yanzu haka an killace mutane 145 wadanda sukayi mu’amala da wadanda suka kamu da cutar domin tabbatar da lafiyarsu.

Har ila yau kwamishinan ya ce baya ga wadancan, sun samu kira har guda 9 daga al’ummar gari wanda yanzu haka suke kan bincike akai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!